Tuesday, 3 December 2013

BABU MASU AIBATA MINISTER YERIMA SAI 'YAN ADAWA MASU YARFEN SIYASA

Dr. Yerima Lawal Ngama dan asalin jihar Yobe a garin Gashua, Kamar yadda kowa ya sani sunansa ya shahara ne a fagen aikin banki musamman a bangaren kasafin kudi, ko da ya ke dama ya yi digirinsa na farko a kan aikin Akawu a Jami'ar Maiduguri, ya sake yin digirinsa na biyu a fannin Akawu da kasafin kudi, a Jami'ar Glasco da ke kasar Ingila, ya yi digirinsa na uku a fannin kididdigar kudi da kasafinsu a Jami'ar Birmingham da ke kasar Ingila.
An ruwaito cewa minista Ngama mutum ne mai kwakwalwa tun yana karamin yaro, bai taba wuce mataki na uku a ajinsu ba, ya tab'a karbar lambar girma na Zakaran dalibi a Gashua Central Primary School a 1973. Ya sake karbar kyautar dalibin d'alibai a Govt Secondary School Gashua a 1978. Ya sake karbar kambun karramawa ma fi girma wanda ya rubuta kundin bincike a 1990 a Jami'ar Birmingham a kasar Ingila. Babban bankin Najeriya ya karramashi da kambun girmama basirarsa a 1991. Haka Diamond Bank wanda ya karrama shi har a karo na biyu. An bayyana cewa ministan ya fara da aikin koyarwa ne a Jami'ar Maiduguri fannin tsimi da Akawu, har zuwa lokacin da ya zama babban malami a sashen, ya yi zaman bincike a Tulane University, New Orleans a Kasar Amurka. Sannan ya yi aiki da Nigeria Deposit Insurance Corporation a matsayin babban Manager a sashen tsare-tsaren gudanar da bankuna. Dr. Yerima ya rike mukamai a bangarori da dama a 'Diamond Bank' wanda suka hada da manajan shiyya-shiyya da shugaban gudanarwa da kuma babban darektan harkokin walwalar jama'a. Kafin daga bisani ya sauya akalar aiki zuwa First Bank in da a nan ya rike babban darektan na shiyyar Arewa.

An tantance shi ne cikin rukunin wasu mutane da dama in da a ka tabbatar da dacewarsa na zama ministan kudi, a wancan lokacin kuwa minista Ngozi ba ta bar mukaminta na babban bankin duniya ba, a sannan ne kuma takaddama ta kaure wasu na ganin Dr. Yerima ne ya fi cancanta ya zama babban minista yayin da wasu ke ganin ai Ngozi ce ta fi dacewa.
Daga bisani a ka yi maslaha a ka ba shi karamin minister ita kuma babba.
Sanin kowa ne mulki ya na da wuyar sha'ani a Najeriya musamman wajen wadanda su ka rike gaskiya da amana.

An ruwaito cewa tun da minista Yerima Lawal Ngama ya kama aiki ya samarwa mutane da yawan gaske aiki a fannoni da dama kuma yana tallafawa matasa wajen samar da sana'o'i da ayyukan dogaro da kai. Kasancewarsa mutumne mai kaunar talakawa ya zamto linzamin janyo duk wani aikin alheri daga gwamnatin tarayya zuwa yankunan Arewa.
An bayyana ministan a matsayin mai aikin gani a k'asa ba yawan surutu ba, nazari da bincike sun nuna cewa ya na kishin al'umma fiye da yadda ya ke kishin aljihunsa da muradunsa.

A satin da ya gabata ya bayyana cewa da 'yan majalisar tarayya sun rattaba hannu a kasafin kudin 2014 to, da al'amura sun saukaka ga al'ummar kasar nan Kuma da ba a samu tsaikon gudanar da kasuwanci ba saboda walwalar kudi a hannun al'umma. Wasu 'yan adawa tuni su ka juya wannan al'amari su ka fara sukar wannan ra'ayi a wasu kafafen yada labarai, to, wani abu da Hausawa su ke cewa Allah ke gadin shekar Tsuntsu ba iska ba in don ta iska ne da tuni ta yi tafiyar yaji da shi. Wasu kuwa na cewa in Hasken Rana ya fito tafin Hannu ba ya iya kare shi.

Mu dai kullum cikin fatan alheri mu ke ga shugabanninmu na gari, wajen da su ka kuskure Allah ya yi musu jagora zuwa hanyar haske.

No comments:

Post a Comment